☘️☘️☘️☘️☘️ *SAI YANZU❔* 42 ☘️☘️☘️☘️☘️



           *NA*

 

       *HANNE ADO ABDULAHI*



(¯`*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿`°¤,¸.•*´¯)


 

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү  α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.


INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/


FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/


TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09



CHAPTER FORTY TWO

 Alhamdu Lillah aure dai ya dauru tsakanin Zarah da Faruk. Gudun ma kar Mommy ta sake kawo masa matsala ya tattara yaransa da sabuwar amaryarsa suka koma Warri.

 Da farko an dan so samun matsala, amma daga baya ya samu ya lallabe ta ta karbi kaddarar da Allah ya sakko musu. Hakan ya sa Zahra ta rungumi aurenta da kuma marayun yaran da uwarsu ta mutu ta bar mata da hannu bibiyu.

 Shima Ibu a nasa bangaren ya dau ta sa amaryar watau Humaira suka koma Lagos in da ya ke aiki. Sai da hutu ya kare san nan ta koma Abuja saboda karasa karatun ta.

 A bangaren Baffa ne dai akwai matsala tsakaninsa da Abbansa, saboda sama da wata biyu da sakin wulakancin da ya yi wa Sofi, Abban nasa baya amsa gaisuwarsa. Sallama ce kawai ya ke amsa masa daga ita ba kari.

 Ga aiki da ya sako shi a gaba ba kama hannun yaro, saboda sun fara hada jiragen da suka kero daga Japan. Kusan kwana suke a wajen aikin na su.

 Kanon ma ba sosai ya ke samun lekowa ba. Amma a dan lokutan da ya kan shigo ya kasa samun kan Abban nasa. Fushi ya ke da shi sosai.

 A bangaren Honourable ma kuwa al’amarin nasa sai hamdala. Saboda wahala dai ya na shan ta. Momi ta watsar da shi neman kudi kawai ta ke da ciwonsa.

 Dan abin da ta samu ta karar da shi a wajen Sofi saboda ta dage sai ta daga darajar yarinyar ta samo mata miji dan gayu mai kudi. Ta kuma yadda hakan ba zai yiwuwa ba sai ta kashe kudi wajen daga darajar ta. Ta kan ce mata “sai da kudi ake neman kudi”.

 Shi kuwa marar lafiya saboda ta ga bashi da amfani ta watsar da shi. Dan lokaci kadan ta kan kira Saddam taji ya jikin nasa. Dan abin da ta kan turawa Saddam din shi ma ya yi gararin gabansa da su.

 Ba bu wanda ya ke jin ‘kan sa a cikin iyalan da shi ya kashe rayuwarsu wajen kyautata musu da biyan bukatarsu.

 Ran Mallam Jibo bai taba baci da Baffa ba, irin wan nan rana. Asibiti yaje duba wani abokinsa. Su na cikin gaisawa ya ji kamar gurnani a bayansa.

 Ya juya nan ya yi arba da wani dattijo da gani yana jin jiki. “Sannu bawan Allah. Allah ya baka lafiya” Mallam Jibo ya ce da shi.

 Amma sai yaga dattijon kamar yana son magana da shi. A lokacin daya kuma abokin nasa ya ke bashi labarin matsanancin halin da mai jinyar ya ke ciki saboda watsi da shi da iyalinsa su ka yi da shi. Ashe na sa mai jinyar ne ke taimaka ma sa ya kula da shi. Ashe hatta kudin magani shi ya kan taimaka ma sa da shi.

 Gaban gadon ya karasa sosai domin duba marar lafiya ya kuma dan yi masa alkhairi, sai ya lura mai jinyar ya na kallonsa yana hawaye. Yana kura ido da kyau sosai sai yaga ashe Honourable ne.

 “Inna Lillahi wa inna ilaihi raji’un” shine abin da mallam Jibo ya iya furtawa.

 Shi kuwa da hannusa daya mai lafiya ya kamo hannun Mallam Jibon ya rike, hawaye na dada kwarara daga idanunsa.

 Shi ma hawaye ne ya zubo daga nasa idon. Sai fadi ya ke “wallahi Yaya ban san baka da lafiya ba”.

 Bai samu damar amsa tambayar da abokinsa ya ke masa ba,  ya nufi ofishin mai kula da dakin majinyantar.

 Nan ya samu cikakkaen bayanin ciwon da ya ke damun Honourable. Yaji takaicin wai har bashin kudin gado ake bin Honourable.

 Ba tare da bata lokaci ba ya biya bashin kudin ya kuma samu aka bashi daki na mutum shi kadai. Walid ya buga wa waya yazo ya same shi a asibitin shi ya aika ya sayo musu duk abin da ya san za su bukata. San nan ya barshi ya zauna da shi, shi kuma ya koma gida domin ya dan kimtsa ya dawo zama da shi.

 Shi ya dawo kula da shi. Wabili kuma ta ci gaba da zuwa duba su tare da dawainiyar abincin mai jinya. Ya yi zama na kwana ya kai hudu amma bai ga keyar Saddam ba da aka ce shi ne mai jinyar Honourable.

 Baffa yana tsaka da aiki ya ga wayar Mallam Jibo, katse komai ya yi ya dauki wayar. Cike da girmamawa ya gaishe shi, amma Mallam Jibo ya katse shi da fadin “in ka samu lokaci kazo ina neman ka”.

 Ya na fadin haka ya katse wayar. Da rawar jiki Baffa ya bar duk aikin da ke gabansa ya tafi neman jirgi zuwa kano. Awa hudu tsakanin kiran Abbansa da kuma isowarsa gida kamar yadda Abban nasa ya bukaci ganinsa.

 A ganin Baffa babu wani aiki da ya fi karfin ya jingine shi domin amsa kiran Abbansa.

 Amma tashin hankalin da ya tarar ba karami bane. Ya na isa gidan Abba bai saurare shi ba, ya aika aka kira mai unguwa da Mallam Liman da kuma abokin mahifinsa Alhaji Sule mai shayi.

 Baffa ya rasa wan nan ganganmi na menene. Amma tashin hankalin da Baffa ya fuskanta bayan isowar dattijan ba kadan bane.

 Abba ne ya sauka daga kan kujerar da yake zaune ya durkusa gaban Baffa, san nan ya ce “Engineer Ahmadu ina son in roke ka alfarma. Ka yi wa girman Allah ka kula da Yaya Iliyasu ko kuma ni ka daina yi min duk wata hidima ka dauki nauyin wan mahaifinka.

 Idan kuma har ka na ganin ba za ka iya min wan nan alfarmar ba to ni zan bar maka gidan nan ka dauko shi ka dawo da shi nan da zama”.

 Baffa daskare wa kawai ya yi a zaune kafin yayi sa’a wani zazzafan hawaye ya zubo masa. Sai a san nan ya samu bakin Magana yace “Don Allah Abba kayi hakuri kar kasa la’anar Allah ta hau kaina. Wallahi na yarda duk abin da kake so zan yi maka shi, amma Abba ka yi hakuri ka daina zubar da hawayenka a kaina”.

 Su mallam Liman ne suka shiga ba shi baki shi kuwa ya nuna musu matso Baffa ba zai daidaita da Honourable ya manta abin da ya faru a baya ba, to shi ma kuwa ya yafe shi ke nan har abada.

 A wan nan rana duk kansu suka je duba Hohourable. Shi kansa Baffa duk da haushin abin da Daddy ya yi masa amma hakan bai hana shi jin tausayin halin da ya ganshi a ciki ba.

 Hutun gaggawa ya dauka na kwana uku. A wadan nan kwanaki kuwa sai da ya sa mai unguwa ya nemo masa wanda ya sayi gidan Honourable lokacin da biyan diyya ya hau kan Sofi.

 Ya dora masa dan wani abu ya yarda ya sayar masa da gidan. Shi kuma ya saye shi a sunan Daddy. A kwana ukun da yayi ya nunawa Daddy kulawa bata wasa ba. Sai dai duk sanda ya shiga asibiti wajensa ba ya iya komai sai kuka. Har ran nan Baffan ya gaji ya ce “ina ga dai daddy ba ka son ina zuwa dubaka”.?

 Girgiza masa kai alamun ba haka bane sabo da har yanzu da jikinsa ya dan yi kyau ba ya iya Magana. Baffa ne ya ci gaba da cewa “to in dai ba haka ba ne ka dai na kuka idan ka ganni”.

 Da sauri kuwa ya daga kansa alamun ya daina. Dan zaman da ya yi na kwana biyu shi ya ke masa komai shi da Mallam Jibo hatta kwana shi Jibon ne ya ke kwana da shi.

 Ranar da ya zo zai masa sallama saboda dole ya koma bakin aiki sai a ranar ya hadu da Saddam. Saboda tun da Mallam Jibo ya canza masa daki bai samu zuwa ba sai yau.

 Shima dan kudi ya samu Mommy ta tura masa saboda ta raka wata ‘yar kawarta da zata je haihuwa a Dubai. Sofi kuma ta zauna mata da yaranta a gida.

 Ga nasu mai larurar sun yar a gida amma sun tafi yawon raraka.

 A wulakance Saddam ya gaisa da shi saboda har yanzu yana jin haushin hana shi Zara da ya ke ganin Baffan yayi.

 Shi ma kuwa bai bi ta kansa ba, sai da ya ga shi Saddam din ya doshi babban daki inda marasa lafiya da yawa ke kwance san nan ya ce “idan Daddy kake nema yana Ammenity 1”. Daga haka bai kara ce masa komai ba ya wuce ya tafi ya barshi a wajen.

 Ganin dakin da aka canza wa Daddy mai kyau ne ba takura ko kadan ga kuma kayan ciye ciye iri sai ya dawo da zaman a dakin. Amma fa ba ya yiwa baban nasa komai.

 Mallam Jibo ne ke dawainiya da shi. Doguwar kujera ya samu ya mai da ita wajen kwanciyarsa. Ga socket na cajin waya ga wuta ko da yaushe sai zaman ya masa dadi.

 Nan zai wuni shiga yanar gizo gizo ba neman abin da zai amfane shi ba sai kallace  kallacen banza da na wofi. Ko kuma ya bata lokaci buge bugen game.

 Daddy yana samun kulawa matuka. Domin hatta Zarah da Humaira sai da suka zo duba shi. Ranar da Saddam ya ga Zahra ba karamin bakin ciki ne ya kamashi ba, saboda yadda ta dada hadewa ta zama hakimar mace.   Kwarjinita kawai ya hana shi ya yi mata ko da Magana ne, duk kuwa da tanadin cin mutuncin da ya yi niyyar yi mata a duk lokacin da su ka hadu. Amma ga shi sun hadun ya kasa kallon ko kwayar idanunta balle ya samu karfin halin yi mata tijara. Sai ita ce ta daure ta fara gai da shi.

 Daddy kuwa murna kamar me. Duk da maganarsa bata fita, amma tabbas su Zahra sun fahimci kalmar hakuri da ya ke ta maimaitawa a lokacin da ya riko hannayensu duk su biyun.

 Hamida kuwa ita ke dawainiya da abincinsa da kuma na Mallam Jibo da Saddam. Bayan an sallamo shi daga asibitin Mallam Jibo ya mayar da shi sashen baki na gidansa saboda ya ji dadin kula da shi.

 Likitan asibitin shi ya basu sunan wani babban asibiti da suke gashi saboda masu larurar shanyewar barin jiki, amma fa da tsada, saboda irin na’urorin da suke amfani da su.

 Nan fa Baffa ya saki makudan kudi aka ci gaba da kula da lafiyar Daddy. A lokaci guda kuma ya bayar da kwangilar gyaran gidan Daddy tare da sanya masa kayan gida a ciki.

 Da kyar Baffa ya samo labarin Amir wanda tun da larurar Dady ta faru ba wanda ya ji duriyarsa, ashe wai ya na kulle a gidan yari.

 Lawyer da Baffa ya dauka shi ya sanar da shi abin da ya faru. Sun yi fada da wani mutum ya soke shi da wuka. Allah ya takaita mutumin bai mutu ba.

 Saboda rashin wanda zai yi ko belinsa ya sanya aka tura shi fursuna na wata goma.

Baffa bai yi kokarin fito da shi ba, amma yayi kokari ya sanya aka canza masa wajen zama a prison din, in da ya samu aka ba shi dakin da ake aje manyan mutanen da duniya ta juya musu, ya kuma yi amfani da wan nan damar ya ba shi kulawa saboda shaye shaye da ya yi masa karo. Likitan da ya kware da warkar da ‘yan shaye shaye ya samu ya ke zuwa duba shi tare da ba shi duk kulawar da ta dace da shi.

 Kafin lokaci kankani kuwa an samu ya dawo hayyacinsa.

 Mommy kuwa sai da ta dauki sama da wata biyu san nan ta dawo. Saddam kuma da ta dawo bai yi hankalin sanar da ita ci gaban da aka samu ba. Saboda da duk alkhairin da Baffa ya yiwa mahaifinsa bai sa ya dai na jin haushin hana shi auren Zahra da yayi ba.

 In ban da rashin hankali ba abin da Saddam ya ke zubawa. Tare da shi da Daddy suka koma gidan Mallam Jibo da zama. Amma ko gaisuwa ba ta hada shi da kowa a gidan. Wai shi ala dole fushi ya ke da shi. Amma ana aje tiren abinci shi ya ke fara dira a kansa.

 Daga Baffa har Mallam Jibo kowa ya zuba masa ido ba wanda ya ke bi ta kansa. Shi Saddam haushin Daddy ya ke ji idan ya ga rawar jikin da yake idan Baffa ya zo ko ya bugo waya. Ko kuma ya ga yadda ya ke mutunta Mallam Jibo.

 Saboda wadan nan dalilai na sa, ya sanya bai sanar da Mommy halin da su ke ciki ba

Hakan ya sa sai da ta sake zaman wajen wata a Abuja.

 Ta dai yi nasarar samowa Sofi miji mai halin da ta ke so. Dan wata kawarta ne aka hada su. Hakan ya sa ta dawo saboda shirye shiryen biki.

 Ta nemi Saddam ya sanar da ita ai Baffa ya sai masu gidansu na da sun koma. Daddy kuma ta same shi jiki da sauki sai dai yana takawa da sanda.

 Kwarai tayi murnar ganin Baffa ya jibanci lamuransu. Nan kuma ta zauna shiryawa Daddy yadda zasu mallake Baffa su kadai ko don hidimar auren Sofi da ta tunkaro su.

  Daddy ba karamin haushinta ya ke ji ba. Sai yanzu ya gane Mommy ba abokiyar zaman arziki ba ce. Sai yanzu ya fahimce Mommy ba mace ce mai iya dora mijinta akan hanya ta gari ba.

 Sai yanzu ya lura Mommy ba ta taba kaunar danginsa. Sai yanzu ya san ya tafka babban kuskure wajen biye mata ya zubar da nasa dangin.

 Gashi yanzu da larura ta same shi dan da ya banzantar shi ya dawo ya taimake shi. Sai yanzu ya yarda da Karin maganar bahaushe da ya ce “da da dukiya ba a yi musu mugunta, saboda ba a san wa za su amfanawa ba”.

 Ga dai dan da ya wulakanta ya tozarta iyayensa shine a yanzu ya tallafe shi ya taimaki rayuwarsa.

Bai dada godewa Baffa ba sai ranar da ya gayyace shi suka je prison domin kaiwa Amir ziyara. Ga shi nan ya zama mutum sosai. Alamun sun nuna in Sha Allah shi da shaye shaye sun yi ban kwana.

 Ya yi kyau ya murmure. Kammanninsa na asali sun fito. Saboda hatta abinci mai rai da lafiya ake ba shi a cikin prison din, wanda ka’ida ne sau uku a rana a bawa direban Mallam Jibo ya kawo masa. Sai gidan yarin ya koma masa kamar wajen warkar da ‘yan shaye shaye ba wajen tsare masu laifi ba.

 Duk sati kuma ka’ida ne Malla Jibo ya kai masa ziyara da kansa. Nan kuma zai bata lokaci yayi ta kokarin nusar da shi irin rayuwar da ta kamance shi wacce kuma ita za ta taimake shi ya zama kamilin mutum.

 Shi ma Amir a nasa bangaren yana daukan nasihar Mallam Jibon da muhimmanci. Ko ba komai daukakar da Allah ya yiwa Baffa ta na burgeshi.

 Sai ya kasance ba ya son abin da zai yi ya bata ran Baffa. Baffan kuwa ya nu na masa in dai zai koma shaye shaye to kuwa watan batawarsu ya zo.

     ****************




CHAPTER FORTY THREE

 To Mommy dai Allah ya taimake ta an sako amir daga fursuna. Bayan ya shafe kimanin watannin takwas a gidan yari. Ganin alamun nadama a tare da shi ya sanya kotu ta yafe masa sauran watannin biyun.

 Baffa ne ya dauko shi da kansa. Bai kuma kai shi gaban iyayensa ba, sai da ya barshi ya kwana biyu a wajensa. A dan wan nan lokaci kuwa ya sha jarraba shi ya gani ko da gaske ya daina shaye shaye.

 Amir kuwa ya tabbatar masa da Allah ya taimake shi ya yi bankwana da kwaya. Ya saya masa suturu na kamala domin ya fi son iyayensa su gan shi a cikin kyakkyawar kama.

 Ba karamar murna Honourable ya yi ba ganin babban dansa ya shiryu. A wan nan rana ma kuwa sai da Baffa ya nuna masa bacin ransa saboda kuka da rokon gafara da Daddy ya ringa yi.

 Yin hakan ya kular da Mommy saboda har yanzu ta ki karbar laifin ta. Har a wan nan lokaci tafi ganin Baffa shi ya janyo musu halin da suka samu kansu a ciki.

 Ganin rawar jikin da Daddy ya ke yi wa Baffa ya sanya ta tabe baki ta ce “shiriya dai ta Allah ce ba ta mutum ba. Balle a yi inkiyar wani na shiryar da wani”.

 Daddy bai bata lokacinsa musu da ita ba. Saboda ya fuskanci zuciyarta a bushe ta ke. Bai kuma ga alamun zata sassauta ra’ayinta akan kiyayyar da ta kewa Baffa ba.

 Saboda lokuta da yawa idan taga Daddy yana kakabin wani abin alkhairi da Baffa yayi mu su sai ta dinga yada Magana ta na fadin “Sofin ma dai Allah ya tarfa wa garinta nono. Tun da wanda zata aura ba aiki yake a karkashin wani ba. Gashin kansa ya ke ci”.

 Daddy ba ya tanka mata tun da ya fahimci rashin amfanin hakan. Saboda ya gane har yanzu bata hankalta ba. Ga wani abin alkhairi da Baffa ya yiwa Amir. Lokacin yana fursuna wani abokinsa da su ka yi jagaltun rayuwa tare, Allah ya yi masa rasuwa.

 Ya mutu ya bar matarsa da karamin yaro da kuma tsohon ciki. Tun da Amir ya fito daga prison ya samu labarin rasuwar abokinsa ya shiga tashin hankali matuka, wanda hakan ya dada rusunar da zuciyarsa. Dumbin nadama ya dada shigarsa.

 Ganin da Baffa yayi Amir ya mayar da hankalinsa wajen kula da iyalin abokinsa da kuma yawan yabon matar da ya ke yi. Yana yawan bashi labarin hakurin da kuma ilmin addini da take da shi. Ya kan ce masa “duk iya shegen da za mu yi a gabanta sai dai ta yi kuka ta share hawayenta ta bi mu da addu’a. ko kara ba ta taba kaimu gidansu ba. Kullum ta kan ce Aliyu kaddarar rayuwarta ne. ta kuma karbi kaddararta ta”.

 Baffa y ana sauraron yadda yake yabawa Shuhuda matar marigayi Aliyu abokinsa. Hatta awo zuwa asibiti Amir ne ya dauki nauyin kai ta da kuma daukar duk dawadiniyar ta da ta karamin yaronta dan shekara biyu mai suna Yusuf.

 Ga shi dai a lokacin ba wani abu ya ke yi ba, amma dan tallafin da Baffan ya ke ba shi a kan Shuhuda ya ke karar da shi. Ranar da ta haihu ranar Baffa ya ganta. Karamar yarinya da ba za ta haura shekaru ashirin da haihuwa ba. Duk da yanayin rayuwa, amma hakan bai hana kyawunta bayyan ba.

 Baffa kuwa ya na ganin inda hankalin yayansa ya koma kan Shuhuda sai ya saki bakin aljihu ya bawa Amir isassun kudi ya yiwa maijego da danta sayayya. Ranar sun jariri yaci sunan mahaifinsa watau Aliyu sai ake masa lakabi da Haidar.

 Hidimar sunan ma duk Amir ne ya yi ta. To hakan ne ya bawa Baffa damar ba wa Amira shawarar ya aureta ya rike mata marayun yaranta.

 Tare suka samu Daddy da wan nan shawara. Shi ma kuma yayi farinciki da wan nan shawara. Ko ba komai ilmin da tarbiyya musulunci da ya kasa bawa Amir, yanzu zai samu mai wan nan ilmi, saboda mahaifin Shuhuda kowa ya san shi babban malami ne.

 Shi ma abokin nasa da ya rasu saboda yar uwarsa ce shi yasa ya samu nasarar aurenta. Kuma tabbas ta yi hakuri da shi da sakarkarun abokansa. Kullum cikin adduar shiriya a garesu ta ke.

 Duk da Mommy ba ta nuna goyon bayanta akan auren ba, saboda it aba irin Shuhuda ta ke bukata a mtsayin surukarta ba. Ta fi ‘yar masu kudi ko masu Mulki wadanda sunansu ya yi fice da samun abin duniya. Duk da haka Daddy ya tsaya musu matuka. Baffa kuwa ya saya masa gida dan madaidaici ya shirya masa shi suka tare shi da amaryarsa Shuhuda da yaranta guda biyu.

 Da farko iyayenta sun so su dauke yaran har da jinjirin da ta Haifa, amma Amir ya nuna sam ba zai yadda ya bayar da rikon yaran amininsa a wani waje ba. Ban da gida Baffa ya bude masa super market mai dan girma ba laifi. Kuma Alhamdu Lillah ya rike iyalinsa da kuma wajen neman abincinsa da muhimmanci.

 Baffan ne dai da ya samu labarin auren Sofy da za ayi daga wajen Daddy. Bai gaji ba ya dunkula makudan kudade ya bashi domin hidimar auren. An yi ta bin Ango ya nuna gida ya ce ba a gama ba. Mommy kuwa aka sayi kayan gidan amarya da yawa kamar na amare uku. Sauran kudin ta hada gaggarumar dinner.

 Hall ma na bikin sai da aka biya wajen miliyan biyu kudin hayarsa. Banda abinci da abinsha na bajinta. Aka yi haddaadiyar dinner. A nan ta murkushe fiye da rabin kudin da Baffa ya bayar.

 Washegarin dinner aka daura aure sai kuma a lokacin ango ya nuna gidan da za a kai amarya. Akwatance da ya yiwa mommy yace a Darmnawa ya ke gini. Ta dauka wajen da ake kira sabuwar Abuja ne. sai da su ka je su ka tarar ashe a dan tsinke ya ke.

 Irin kwatan fulotin nan ne aka kwakuba dakuna guda uku. Bandaki da kitchen kuwa in dai ta shiga sai dai ta fito da ribas. Sai kuma a lokacin gaskiyar lamari ta fito. Ashe wacce ta ce mata danta ne ba haihuwarsa ta yi ba. Almajirinta ne ta yi masa riko mai kyau.

 Mommy hauka ne kawai ba ta yi ba. Daddy kuwa ya ce aure ya dauru ba wanda ya isa ya hana ango tafiyar da matarsa. Haka aka kaita dan takurarren gidanta wanda saitin gadon ma ya ki shiga dakin. Sai a wani dakin aka saka mata sif da madubinsa.

 Da farkon zuwa ta so ta nuna masa rashin kunya da haukan fashe fashe da ta saba yi a gidan ya kama ta ya nada mata duka. Tun daga lokacin ta ke shakkarsa.

 Ga wata babbar illa da Habib mijin Sofi ya ke da ita. Tsumulmula kamar zunbuli. Balle da ta yi rashin sa’a Mommy ba ta samu sukunin yi mata gara ba, ta fake da haushinsa ta ke ji na yaudarar da ya yi musu, amma alal hakika babu kudin garar ne saboda ta kadar da su a kayan daki da kuma shagalin biki.

 Hakan ya gadar wa da Sofi gori a wajen Habib. Ga shi abin kamar sihiri tsoronsa ta ke kamar mutuwarta. Ya hana ta karatu ga dan banzan kulle ba inda ta ke zuwa. Hatta kallon talabijin yana da doka ba akallon komaia gidansa sai tashar ball.

 Haka za ta zauna ko ‘yan wasan ba ta iya shaidawa, amma saboda ta samawa kanta lafiya idan ta gay ana murna club dinsa ya ci haka za tai ta murnar da ba ta san dalilin yin ta ba. Idan kuwa aka cinye club dinsa ranar ta shiga uku. Wuni zai yi yana fushi da zage zage.

Duk wanda ya san Sofi idan ya ga yadda ta koma sokuwa sai yayi mamaki. Duk izza da jin kan nan na ta, Habib ya sauke mata shi. 

 Saddam kuwa ta sa kaddarar ta sanadin matar da ya aura ne. masifa gareta kamar sauro. Gata yar figigiya da ita, amma shakkar ta yake kamar uwarsa. Balle da ya ke ita tana aikin asibiti, shi kuma ba ya komai sai rainin ya dada yawa.

 Shi ma dai Baffa ya saya ma sa gida, dan jarin da ya bashi ya murkushe shi. A wajen Amir ya ke samun dan na kashewa, wanda shi kuma shi Allah ya tarfawa garinsa nono.

 Gaba daya Mommy a cikin tashin hankali ta ke saboda matsalar Sofi da ta Saddam. Ga ciwon girma da ya sakota a gaba. Ga tsabar bakin cikin Baffa da kannensa da ke nukurkusarta.

 Yan biyu kowacce ka ganta gwanin sha’awa. Balle Hamidan ya Baffa autar mata. Ita kuwa tata ‘yar da ta daukaka sama da kowa ta koma abar tausayi. Ko ruwan pure water idan ka ziyarci gidanta tsoron baka ta ke yi, saboda mai gidan kirgawa ya ke yi.

 Baffa kuwa Allah ya taimake shi aikin da aka bawa kamfaninsu ya kammala, bayan shekaru biyu da suka kwashe suna aikin. Bayan sun kammala aiki gwamnatin tarayya ta hana shi komawa Japan saboda ana bukatar ya zama mai kula da kai kawon sabbin jiragen.

 Duk da haka sai raba kafa ya yi saboda suma kamfanin na sun a can Japan sun ki sakinsa. Sai ya ringa kai kawo a tsakaninsu. Sai ya dada sa’a gwamnati ta bawa kamfaninsu gyara da kula da jiragen na tsawon shekaru biyar. Shi din dai kamfaninsu ya wakilta ya ci gaba da wan nan aikin.

Hamidan sa ta Haifa masa dansa mai sunan Abba watau Jibir sai suke kiransa da Shahid. 

 Zara ma ta Haifa wa su Sadik kanwa wacce ta yi wa yayarta marigayiya takwara. Humaira ce ta samu yan biyu dukkansu maza ta yi wa yayanta da surukinta takwara.

 Sai yanzu Honourable ya gane ashe zumunci abin rikewa ne saboda yadda ‘ya’yan dan uwansa suka rike shi kamar mahaifinsu. Sai yanzu ya gane wautar da ya yi da ya biyewa matarsa ya wulakanta dan uwansa da iyalansa. Sai yanzu ya ke dana sanin abubuwan da ya aikata a kan dan uwansa tabbas ya yi nadama ya kuma koka akan abubuwan da suka faru

   Momi kuwa lamarinta sai gyaran Allah. Matsalar Sofi kadai ta ishe ta takaici. Duk da yadda ta so ‘yar ta tata ta daukaka, Allah kuma ba haka ya so ba. Ita kanta Sofin kunyar yadda rayuwa ta koma ma ta, take.

 Daddy kuwa ya murjewa idonsa ya koma jikin Baffa da kannensa. Hatta majalisar dattijai da su mallam Jibo suke zama , nan ya mayar wajen zamansa. Ya shige cikinsu ya yi bulunbukui kamar ba abin da ya taba faruwa na kaskanci a baya.

 Hakan kuma shine babbar matsalar da mata muka kasa ganewa. Lokacin da miji ya ke tsiyacewa da danginsa ki yi uwa kiyi makarbiya ki shiga ciki. Maimakon ki dawo da mijin ki kan hanya sai ki barshi har da gudummowar muguwar shawara. Karshe komai na batanci kan ki zai dawo. Shi kuwa yana komawa wajen danginsa tas za su karbe shi su nuna masa komai ya wuce.

 Allah ya bamu ikon bawa zumunci muhimmancin da addinin islama ya koyar da mu Amin.

Comments

Popular Posts