☘️☘️☘️☘️☘️ *SAI YANZU❔* 35 & 36☘️☘️☘️☘️☘️

 


           *NA*

 

       *HANNE ADO ABDULAHI*



(¯`*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿`°¤,¸.•*´¯)


 

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү  α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.


INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/


FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/


TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09



CHAPTER THIRTY FIVE

 Baffa ya rako Ibu da kuma wani abokinsu wanda shi kuma lawyer ne, mai suna Idris Goni. Daga dukan gate din da aka yi su ka san ba lafiya ba.

 Buba maigadi ya dauko gora daga dakinsa ya nufi gate din yana fadin “Yallabai ku koma daga ciki ina ga barayi ne”.

 Ba su saurarin maganr sa ba suka nufi gate din dukkansu. Ta dan yankan da ya kan leka domin ganin waye sai kawai yaga Honourable. Ganin haka ya yi saurin bude gidan saboda a tunaninsa wani abu ne ya faru.

 Hankade shi yayi ya nufi cikin gidan yana kiran police din da suka taho tare da shi da su shigo cikin gidan.

 Bai kula da su Baffa a gefe ba saboda bacin rai ya rufe masa ido. Falon gidan ya nufa yana kwalawa Mallam Jibo kira.

 “JIbo fito munafikin Allah. Yau zan nuna maka ko ni waye. Tun da kana jin kayi jan wuya da zaka iya munafunta ta”. Da karfi Honourable ya ke magana mai nuna tsananin fushin da ya ke ciki.

 Baffa, Ibu da kuma Idris mamaki ya hana su motsi, sai kuma ga Baffa Petal da su Bawuro da kuma Mallam Jibo sun fito suma da sauri saboda jin tashin muryar Honourable da wan nan tsohon dare.

 Ba dan ma biki aka yi a gidan ai su da sun dade da shiga barci. Honourable na hango Mallam Jibo ya nufe shi da sauri. Yana zuwa ya shaki wuyan rigarsa.

 Wani irin zagi ya ke dura masa kamar tsohon bamaguje. Baffa Petal ke fadin  “sake shi Iliyasu. Koma menene ba zai zamo abin da zai gagara ba”.

 “Kar ka ce da ni komai. Kai ma ai dattijon banza ne. Tun da akan idonka aka mallake min da na” Honourable ya fada cike da bacin rai.

 “kai kado ki kiyaye harshen ka kar in raba ka da shi yanzun nan. Baffanmu ba sa’an ka ba ne da har za ka zage shi” Ba wuro shi ma ya fada a harzuke.

 Ibu ne yayi niyyar isa in da suke Baffa ya rike shi ya ce “kai fadan manya me ya kai ka shiga”?

 “AMA ba ka ga abin da ke faruwa ba ne”? Ibu ya gaya masa.

 “Ni kuwa na ga me ya ke faruwa. Ina son mahaukaci ya tonawa kansa asiri”. Baffa ya amsa masa. San nan ya juya ya kalli Idris ya ce “a beg barrister yiwa Commisioner Magana ya tai maka mana da back up don na san daga nan sai police station”.

 “Comon AMA ka bari mu yi koma meye a gida me yasa zamu tonawa kanmu asiri” Ibu ya fada.

 Sai da ya yi dariyar keta san nan ya ce “ai shi da ya zo tsokana shi ya taho da police din don su tafi da Abbana, and kana ganin zan kyale shi”?

 “kuma fa hakane” Idris ya fada yana mai kokarin zaro wayarsa daga aljihu.

 Ba tare da wani jinkiri ba ya kira yayansa wanda shine sabon police commissioner da aka kawo jihar nan.

 Atakaice ya zayyana masa bukatarsu. Ai kuwa hasashen Baffa ya zama gaskiya domin suna karasawa wajen su mallam Jibo suka tarar da Honourable yana bada iznin police din da ya zo da su su tafi da shi.

 Police din na kokarin cakumarsa Idris ya ce “dakata officer haka ake kama mai laifi”?

 Police din ya juyo a fusace ya ce “kaga mallam idan ba kaima kana son in hada da kai ba ka barni inyi aikina”. Ya na fadin haka ya sake juyawa da niyyar damkar mallam Jibo.

 Baffa ne ya rike hannunsa san nan yace “ba dai ina raye ba”.

 Nan dai hayaniya ta barke tsakaninsu. In da shi Honourable ya dage sai an kulle Mallam Jibo amma Idris da Ibu da kuma Baffa sun hana Police tafiya da shi.

 A tuaninsa kawar da Mallam Jibo daga kusa da Baffa shi zai ba shi damar lankwasar Baffan ya amince da bukatarsa. Saboda ya hakkake a zuciyarsa shi Mallam Jibon ke zuga Baffa yana bijire ma sa.

 Hamida da ke sashenta da kuma su Wabili da ke can cikin gida ba su san me ke faruwa ba, saboda karar AC da kuma nauyin kofofin gidan, wadanda ke hana sautin ciki ya fito ya kuma hana na waje shiga ciki.

 Amsa wayar da Idris ya yi ne ya kawo karshen komai, saboda zuwan Algon guda cike da police.

 Nan take kuwa suka yi awon gaba da Honourable da kuma police din da ya dakko. Sun kama su akan korafin da Baffa ya shigar na kutse a muhallinsu da kuma cin mutunci da suka yi musu.

 Ai kawai sai reshe ya juye da mujiya. Wanda suka zo da niyyar cin mutuncin Mallam Jibo sai komai ya koma kansu.

 A wan nan hayaniyar Baffa ya sulale ya bi su Idris wanda suka je a kan za su bi police din da su ka zo suka tafi da Honourable.

 Duk kokarin Mallam Jibo na ya bisu matasan ‘ya’yan na sa suka ki. Su kuwa daga nan masaukinsu suka wuce har da angon da ya san idan ya koma Abbansa zai tilasta shi ya fito da Honourable.

 Shi kuwa ya yi alkawari yadda mahaifiyarsa ta zauna a bayan kanta to shi ma kuwa Honourable sai ya zauna haka, har ma da ma’aikatan da ya ke takamar ya dauko.

 A masukin bakin na su, su Ibu su ka ga ya baje alamun ba shi da niyyar komawa wajen amaryarsa.

 Ibun ya kalle shi ya ce “ban gane ba? Ba dai a nan zaka kwana ba”?

 Mika yayi san nan ya ce “ka san idan na san na yiwa Abba laifi, kauce masa nake yi har sai na tabbatar hakuri ya rusunar da fushin, sai in tunkare shi da ban baki da kuma gamsasshen bayani”.

 Idris ne ya tuntsire da dariya, san nan yace “watau ka hakura da sayan bakin amarya saboda ka gujewa fadan Abba”.

 “Ni fadan ba zai dameni ba. Saboda babana ne. Idan yana min fada dadi nake ji saboda na san fadan sa duk na in gyaru ne da kuma nuna tsantsan kaunar da ya ke yi min. Amma yau na san tilasta ni zai yi sai na fito da yayan abokinsa.

 Ni kuwa na rantse sai ya dana kwanan bayan kanta ya ji dadinsa. Watakila daga yau idan sabanin ya shiga tsakaninsu da mutane, zai daina kokarin mika su ga police saboda  takamar ya na da abin da zai bayar a kulle su ba tare da laifin su ba”.

 Idris yace “Ni kuma police din na ke son a hukunta min. saboda sun mai da mutane kamar dabbobi. Duk wanda ya fara mika musu dan wani abu to shi za su marawa baya.

 Ta ina aka taba zuwa gidan mutum shi ba rikakken mai laifi irin su sata ko fashi ba, a tafi da shi ba warrant ba komai.

 A doka kafin police ya kama ko mai laifi ne sai ya karanta masa laifin da ake tuhumar sa da shi, san nan ya karanta masa damar da yake da ita na kin yin Magana, saboda da duk abin da ya fada a lokacin za a iya amfani da shi a matsayin shaida a kansa a gaban hukuma”.

 Nan dai suka dan tatauna yadda lamarin kasar nan yake game da harkar kama mai laifi.

 A can gida kuwa Mallam Jibo ya dauka Baffa raka su Ibu ya je ya yi. Sai ya tsaya a farfadar gidan yana dakon shigowar Baffa.

 Ya saka a ransa dole ne ma Baffa da abokansa su sa a sako Honourable. Da kyar su Ba Jauro su ka saka shi ya shiga ciki.

 Amma ko yaya ya ji motsi sai ya leka ko Baffa ne ya dawo. Ya kira wayarsa har ya gaji amma ba ta ko shiga. Sai daga baya ya yi tunanin ko duk suna Police station din ne kuma ya san ba a amsa waya a wajen.

 Bayan ya shaidawa su Baffa Petal abin da ke ransa sai suma su ka dauka hakan ne, saboda haka su ka tafi dakunansu suka kwanta.

 Amarya Hamida kuwa ta gama shirin bacci amma ango bai shigo ba. Ta dan saurara zuwa wajen awa daya amma ta ji shiru.

 Hankalinta ne ya tashi. Ba shiri ta dau waya ta buga masa. Bugu daya kafin na biyu ya amsa.

 “Ai na dauka ba zaki damu da batan mijin ki ba, tun da kin yi niyyar sadaukar da ni” Baffa ya amsa mata wayar.

 Ta dan dada rusunar da muryarta san nan ta ce “ga dukkan alamu komai lafiya a yadda na ji muryarka”.

 “Komai lafiya African queen. Sai ma wani buri nawa da na samu cikarsa a yau. Ba kuma guda daya ba har ma guda biyu”.

 “ko”? shine abin da Hamida ta ce da shi.

 “kwarai kuwa. Kin ga na farko Allah ya cika min burina ya bani ke duk ke din kin so ki gujeni. Sai na biyu na gaya miki idan na dawo”.

 “kai Ya Baffa ta ina na so guje maka? Abban ne ya ce idan nayi abin da ya sani zan taimaki rayuwarka.

 Ni kuma sai naga idan har rabuwa ta da kai zai zamo alkhairi a wajenka, to kuwa zan hakura da samun ka domin kai ka samu wan nan alkhairi da Abba ya yi min bushara da za ka samu”.

 Sai da ya sauke ajiyar zuciya san nan ya ce da ita “watau ina ga African Queen ba ki san zurfin kaunar ki a zuciyata ba.

 Ke ce wadda na kamu da santa tun ranar da kika zo duniya kina tsumman zani. A kanki na fara tambayar Abbana kudi saboda kawai in saya miki abin da kike so.

 Kin san sau nawa Gwaggo na zane ni saboda an zo dukanki na tare bulalar ta sauka a kaina. Kudin da na kashe kuwa a biyan mutane barnar da ki ka yi mu su, da tara su na ke da nafi Dangote kudi.

 Kullum sai an kawo kara garin guje guje kin kifar da bokitin koko, ka an aiki yaro kai nika kin barar da kayan miyar.

 Ban sa da lissafin na cikin gida ba da kike bararwa ina sayo wani in yi replacing kar Gwaggo ta gane ta doke ki.”.

 Dariya ta kwashe da ita. San nan ta ce “kai Ya Baffa. Duk ni kadai ke da wan nan ta’adin”?

 “Ba wani kai ya Baffa. Wuyana saboda daukarki har tsayi na sai da ya ragu, amma duk ba kiyi la’akari da dawainiyar da na yi da ke ba ki ka gudu ki ka barni”.

 “Da na gudu ba gashi ka nemo ni ba. But duk da haka “iam sorry. Kayi hakuri. Da kake ta nana ta min in yarda da kai a kowanne hali ban gane me kake nufi ba sai yanzu”.

 Sai da ya dan nisa saboda jin dadin kalamanta san nan ya ce “na hakura Beuty na. ai kin san ba zan iya dogon fushi da ke ba. Amma kin bar tarihi kina karama. Ga ki da wani irin excess anergy da ba wanda ya san ina ki ke samo shi. Gwaggo sai ta ce wai kamar ana jona miki caji”.

  “Wai ka na ina ne”? Hamidan ta tambayeshi, saboda ta na son bagarar da zolayar da yake yi mata na tuna mata kuruciyarta.

 “Na yi yaji” shi ma ya amsa mata a wasance.

 Shagwabe muryarta tayi san nan ta ce “pls ka yi hakuri. Ya Baffa Midan ka ce fa”.

 Shima cikin muryar rarrashi yace “no ba ruwanki a wan nan maganar. Amma ki yi hakuri don yau ba zan dawo gidan ba. Ki kira Humaira ta zo ta taya ki kwana.

 But pls idan Abba ya tamabaye ki kice masa ba ki san inda nake ba”.

 “Wai don Allah me ke faruwa? Ta tambaya alamun ta tsorata.

 “Ba komai my African Queen. Abba ne ba na son mu hadu saboda na san idonsa idona zai saka ni na yi abin da ban yi niyya ba. And babu ke a cikin maganar”.

 Sun dade suna hira kafin suka yi sallama. Bayan ya ajiye sai ya tuna yanzu hakan ba ta ci abinci ba.

 Mikewa kawai yayi ya fita bayan ya karbi makullin motar Idris. Ya samu wani waje da ake sayar da kaji da tsire ya saya mata. Ya hada da su youghort da apple da kuma Inibi.

 Humaira ya tasa ta zo bakin gate ta karba ya kuma bata umarnin ta je ta taya matarsa kwana.

 Shiga bangaren nasu tayi da ledojin tana fadin “sabon salo kanwar miji da sayen bakin matar wanta”.

 “Kin san mu komai namu daban ne”, Hamida ta amsa mata. Dungure mata kai ta yi tace “wallahi yarinyar nan kin raina ni saboda kawai kin mana overtaking”.

 “Ai yaya Humaira in dai ka samu Ya Baffa ya tsaya maka a rayuwa to ka gama dace”.

 A haka su na raharsu suka ci abin da Baffa ya aiko mu su da shi. Su ka yi kwanciyar su cikin kwanciyar hankali ba tare da sanin badakalar da ake a gidansu ba.

 ****************



CHAPTER THIRTY  SIX

 A gidan Honourable kuwa labari ya sha bam bam. Tun wajen sha dayan dare, Daddy ya fita. Mommy sai ta kalli agogo sai ta ce “Ha ha! Yaro bai san wuta ba sai ya taka ta. Shi da Jibo ya dauka ya isa ya yi jayayya da Daddyn ku. Wane shi”.

 Sai an jima ta sake juyawa ta yi dariyar mugunta ta ce “wai wa ya gano min Jibo na shan kulkin ‘yan sanda”.

 Amira dai tun da ta dawo da ga asibiti ta yi shigewarta daki, ba ta jin dadi, saboda haka ta kanta ta ke yi. Zahra da yaranta na tare da ita.

 “Ni ban damu da dukan wan nan Jibon ba. Kawai ku sa DR AMA ya aure ni” in ji Sofi ta fada cike da tabara.

 Mommy ta jawo ta jikinta ta ce “sha kurumin ki autata. Aure kamar an yi an gama”.

 “Ha ka na ke son ji Mommy na. kuma ina shiga gidansa wadan nan ‘yan biyun da suka nuna ba sa so na. sai na yi maganinsu. Su ma wadan nan bararojin sai sun gane kurensu da su da wan nan yankwananniyar ‘yar ta su”.

 “Duk ki min maganinsu. Ai kin san ni da Daddy duk abin da kuke so zamu samar muku da shi”.

 “Amma Mommy za ki sa shi ya sake wan nan din ko. Kin ga ba na son kishiya” inji Sofi.

 “Tun tuni ma. Ai ki sha kurumin ki. Yadda duk ki ke so haka za a yi. Ni ban zauna da kishiya ai kema kuwa kin fi karfinta”.

 Rungume Mommy ta yi saboda jin dadin maganar ta. Amma bayan da sha biyu ta gota sau Mommyn ta dan fara damuwa, da rashin dawowar Daddy.

 Waya ta dauka ta buga amma aka ce mata wayar a kashe take. Sai ta sake rayawa a ranta suna can ana fafatawa.

 A police station na zone 4 kuwa da ke hanyar BUK, Honourable ya ga wulakanci da bai taba ganin irin sa ba. Su na zuwa aka wurga su cikin cell bayan an tube musu riga. Aka kuma kwace wayoyinsu.

 An bashi dama ya kira mutum biyu kafin aka karbe wayar. Na farko wani dan majalisa ya kira da nufin a nemi commissioner ya sanya a sake shi yanzu.

 Amma shi ma sanin ba wani amfanin da Honourable zai sake yi masa a duniyar siyaysa sai kawai ya katse wayar.

 Na biyu kuwa da ya kira ma kin dauka yayi, saboda wanda Honourable ya kira da farko ya riga ya sanar da shi halin da ya ke ciki.

 Daga shi sai dogon wando na farin yadi da ke jikinsa da kuma singlet din. Cell din in ban da zarnin fitsarin ma su laifi ba abin da ke tashi.

 Ga wasu barayi da aka kamo sun sha duka kamar sakwara. Daya har da bayan gida ya yi a jikinsa. Kuma duk haka akwa gwamutsa su da Honourable.

 Mallam Jibo kuwa ya yi jira har ya gaji ba su Baffa ba labarinsu. Tun yana dakon dawowarsu amma har karfe uku ba a ji duriyarsu ba.

 Hamida da Humaira kuwa bayan sun ci abin da za su iya ci suka adana sauran.

 Washe gari kuwa suna idar da sallar asuba, Humaira ta zaga kicin din cikin gida tayi sa’a su Wabili ba wanda ta fito.

 Ta debi dankalin turawa da kayan miya da su mangyada. A kaskon suyar Hamida na lantarki suka soya dankali. Kajin da Baffa ya kawo musu jiya suka yi wani ragwabo mai dadi dasu.

 Naman kuma suka yanka shi kanana, suka hada source da shi wacce ta sha albasa da kayan kamshi.

 Su ka hada abincin a Kwando mai kyawun gaske suka kira Walid bayan sun tambayi Baffa Hotel din da su ke.

 Walid ya je ya kai mu su abincin. Ya na shigowa gidan suka yi kicibis da Abbansu da kuma su Ba wuro.

 “Daga ina ka ke”? Abban ya tambayeshi.

 “Bakin ya Baffa Ya Hamida ta bani abinci na kai musu”.

 “Shiga ka kaini wajensu”. Shi ne kawai abin da ya fadawa Walid.

 Hotel din LASULTANA suka isa, inda su Baffa suka yi masauki.

 Walid na buga kofar, Ibu ya tambaye waye. Jin Walid ne suka shiga yi wa Baffa tsiya.

 Idris ne ya ce, “ina ga amarya ta sake wani aiken yau zamu sha gara”.

 “Ko kuma ita ta zo da kanta saboda tana kewar angon ba” Ibu ya fada ya na mai bude kofar.

 Dariyarsa ta makale a lokacin da ya yi tozali da Abba da kuma Baffa Petal da su Bawuro.

 Yana kokarin gaishe shi yace “ai ba zan amsa gaisuwarka ba Ibrahimu. Yanzu har kun yi girman da zaku yi min wayo. Ina shi abokin na ka ya ke”?

 Kafin ma ya sake cewa wani abu, Baffa ya bayyana a gabansa.

 Shima yana kokarin gaishe shi ya ce “wuce muje ka fito da bawan Allah da ka sa aka kulle. Daga baya sai in san hukunci da zan yanke maka”.

 Haka nan sum sum suka bi bayan su Abban. Allah ya sani Mallam Jibo bai ji dadin yanayin da ya ga Honourable a ciki ba, sai fadi yake yana “Wallahi ban san abin da suka yi maka ba ke nan Yaya. Don Allah ka yi hakuri ban san abin da su ka yi maka ba ke nan”.

 Shi kam Honourable ya yi laushi. Saboda ko da su Abba su ka zo sai da police su ka kora masa jawabin ya kiyaye harshensa in ba haka ba kuwa su sake sakaye shi.

 Ba karamin muzanta ya yi ba da yanayain da su Mallam Jibo suka same shi a ciki. Da kyar ya danne kwallar bakin ciki da ta taso masa.

 Ya yin da Baffa da kyar ya danne dariyar da ta yunkuro ma sa na ganin halin da Honourable ke ciki. Ya yi laushi kamar kwanannen lettuce.

 Cikin harshen fulatanci Abba ya ba wa Baffa doka da lalle ya janye duk wata kara da yake yi a kan Honourable.

 Nan dai aka sake shi bayan an saka shi ya sa hannu ba zai sake shiga shirgin Mallam Jibo ba.

  Sai misalin tara na safe suka ajiye shi a kofar gidansa, su Abba na dada ba shi hakuri na halin kuriciya da su Baffa su ka aikata a cewarsu. Shi dai bai iya cewa komai ba.

 A cikin gida kuma wani bacin ran ya tarar. Shi yana can yana yaki da sauro da zafi da kazanta, saboda biyar bukatar Sofi amma sai ya tarar da su suna sharar baccinsu.

 Hakan ya sa ya ki tashinsu. Yana kokarin shiga dakinsu, sai ga Saddam ya fito daga kicin dauke da kofin shayi.

 Ya na ganin halin da uban ke ciki sai kawai ya tuntsire da dariya, yana fadin “Mommy ku fito ku ga yadda aka yi wuju wuju da Daddy”.

 Haushi ya turnike shi na ganin rashin kunyar da dan sa na cikinsa ya ke masa.

 Shi kuwa Saddam bai kula ya lura da bacin ran uban ba, ya nufi dakin Mommy ya na kiran “Mommy kizo ki ga yadda Daddy ya koma”. Ya juya ya kalle shi ya sake cewa “Daddy motar diban kwashi ka yi karo da ita. Ka ji warin da ka ke yi kuwa”? Saddam ya fada yana mai toshe hancinsa.

 Bakin ciki ya ishi Daddy sai ga Amir shi ma ya shigo. Shi ma kuwa kamar dayan yanayin da Daddyn ke ciki na dauda da doyi ya fara kakabi. Kuma duk ba tare da nuna tashin hankali na bakon yanayin da suka ga mahaifin na su a ciki ba, sai ma dariyar shegantaka da su ke faman yi masa.

 Yana kokarin shigewa dakinsa, Saddam ya ruga ya nufi dakin Mommy yana fadin “Mommy fito ki ga a yadda Daddy ya shigo kuma wai a haka zai shiga daki. Ki zo ki hana shi kar ya jawo mana wani infection din”.

 Ta idar da sallah asuba ke nan, wadda da ma ba kullum ta ke yin ta kan lokaci ba. Ai kuwa ta na fitowa falon ta yi arba da mijinta cikin kazantaccen hali.

 Ita ma kuwa toshe hanci ta yi tana fadin “Daddy me ye haka. Ka ga yanayin da ka ke ciki kuwa zaka shigo har tsakiyar falo da dauda haka a jikinka.

 Yanzu wan nan carpet din ai sai an kai shi wanki”.

 Takaici ya hana shi Magana. Shi ya na can yana hakilon nemo musu abin da suke so, amma ya shigo ba wanda ya nuna ta shin hankali na yanayi da suka gan shi a ciki, sai ma rashin kumya da yaran da kuma uwar su ke masa.

 Ita ma wacce ake yiwa yakin ta na shigowa ta kalle shi ta ce “Daddy me ye haka? Ina DR AMAn? Ya yarda zai aure ni? Please ka yi sauri ka gyara jikinka kar kayi embrassing di na a wajen mutane.

 A iya tunaninsa duk cin mutuncin da ya yi wa Jibo da Baffa ba su taba yi masa wulakancin da yaran da ya karar da rayuwarsa wajen faran ta musu su ka yi masa a yau ba.

 Bai yiwa kowa Magana ba ya wuce dakinsa kawai.  Bacin rai dai a tattare da shi a wan nan rana ba a Magana.

 Ba su damun da halin da ya ke ciki ba,  matar da ‘yayansa suka kafa majalisi a falon suna kakabi da kuma dariyar yanayin da suka ga mai gidan a ciki.

 Zahra da Amira ba su da labarin abin da ke faruwa, saboda jiya kusan kwana su ka yi Amiran ba ta jin dadi. Sai bayan asuba suka samu suka runtsa.

   Shi kuwa Honourable yana kwance a daki ba abin da ya ke tunawa sai kalamun Baffa na karshe sanda za su rabu inda ya kalleshi cikin idonsa ya yi kasa da muryarsa saboda kar su Abbansa su ji yace da Honourable “Allah ya sa ba bu rabon auren ‘yarka a kaddarar rayuta gaba daya. Saboda in haka ya faru zai zamanto mafi munin kaddarar da na ke jin za ta same ni”.

 Shi kuwa ango ya na isa gida, ya dauki amaryarsa suka gudu daga gidan da sunan za su je yiwa bakin da suka zo musu biki sallama.

 Ba wanda ya san inda suka tafi ga kuma wayoyinsu a akashe. Su Ba wuro sai dariya su ke wa mallam Jibo na ganin wayon da Baffa ya yi masa.

 Mommy kuwa a na ta bangaren ta fara gajiya da nacin Sofi na ita a zo a daura aure. Duk ta bi ta sanar da kawayenta an kusa aurenta da DR AMA.

 Wata daga cikinsu ce ta ce “ ba yayi aure ba kwanaki”.

 “Tun yaushe ya rabu da wan nan local yarinya. Dama babanta ne ya tilasta shi ya aureta kuma Daddy ya sa an saketa” ta shara musu karya.

 AMA kuwa yana can yana hutunsa da amaryasa. Ba su sanar da kowa inda suke ba sai Humaira kawai. Ibu ne yake tsokanarsa ya ce “ko ka takura a bani tawa matar ko kuma in tona maka asiri wajen Abba”.

Comments

Popular Posts