☘️☘️☘️☘️☘️ *SAI YANZU❔* 26 & 27 ☘️☘️☘️☘️☘️

 ☘️☘️☘️☘️☘️

*SAI YANZU❔*

☘️☘️☘️☘️☘️


           *NA*

 

       *HANNE ADO ABDULAHI*



(¯`*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿`°¤,¸.•*´¯)


 

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү  α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.


INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/


FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/


TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09



CHAPTER TWENTY SIX

 Sai da Baffa ya isa airport hakan ya tabbatar masa da shi kan sa  a wan nan rana zai shigo Kano, san nan ya kira Abbansa yake sanar da shi. Saboda ya sai ticket ya kai sau hudu amma ya na fasar tafiyar saboda ayyukan da su ka sha masa kai.

  Abba ya sanarwa da Honourable bayan Baffa ya kira shi, amma abin mamaki a filin jirgin saman su ka same shi. Ga ‘yan jaridu da gidajen Radio da ya gayyato, suna ta zambadawa Honourable tambayoyi. Shi kuwa sai amsa musu ya ke kamar shi ne ma’aikacin Hitachi ba Baffa ba.

 Da yake dan siyasa ne na gaske, ya san yadda zai bagarar da tambayoyin da za su saka shi yaji kunya. Ko kuma su tabbatar wa da duniya bai san komai akan dan da yake ikirari na sa bane.

 Baffa ya yi mamaki kwarai da gaske da ya ga yadda ‘yan jarida suka lullube shi suna kokarin yi masa tambayoyi. Amma shi duk hankalinsa ya na kan neman mutum daya watau Abbansa.

 Jefi jefi ya kan amsa tambayoyinsu. Amma Honourable shi ke katsalandan yana amsa da yawan su. Ya na ta kokarin isa zuwa ga Abbansa amma Honourable ya kanainaiye shi.

 Ga su Amir da Saddam da Mommy da kuma Sofi duk sun zagaye shi sai hotuna suke ta posing ‘yan jarida na daukar su. Kai har da Amira mai tsohon ciki ta taho taryar Baffa. Amma an bar Zahra da ta zamo shakikiyarsa a gida.

  A haka ya samu ya janye shi zuwa wajen motocin da suka zo da su domin taryar Baffa. A bakin motar da Honourable ya bude masa mai nuna alamun shi da shi ne za su shiga kawai ya toge ya ki shiga. Sai waigen waigen neman Abbansa ya ke yi.

 Abba ne ya karaso wajen motar. Duk da sun dade ba sa tare da Baffa, amma kusan duk wasu dabi’unsa ya sansu. Ga yadda fuskarsa ta nuna, ba zai shiga motar wan mahaifinsa ba.

 “Nastu in dilla” Abban yace da shi, watau yana nufin ya shiga motar su tafi cikin harshen fillaci. Ganin in bai yi da gaske ba Baffa niyyar tozarta Honourable ya yi a bainar jama’a.

 Hakan ya sanya shi dan daga muryarsa alamar umarni yake bayar wa. “Nastule”, ya fada masa a dan zafafe.

 A haka rai ba dadi ya shiga motar. Yana shiga Sofi itama ta fada cikin motar, suka saka shi a tsakiya.

 Inda ka san wanda za a kai kurkuku haka Baffa ya bata rai. Duk kokarin jansa da hira da Sofi take yi. Ya kasa amsa mata ko da harafi guda ne.

 Ganin sun dau hanyar gidan Honourble ya saka shi cewa “Daddy dan tsaya ina zuwa”.

“in ma wani abin ne ka bari mu karasa gida mana”, Honourable ya amsa masa.

 Shi da kansa ya umarci driver da ya tsaya. Yana tsaya wa kuwa ya ture kafar Sofi ya fita daga motar. Kafin su gama shanye mamakinsu ya tsallaka titi ya tsayar da dan sahu ya hau zuwa gidansu.

 Da kyar driver ya iya shanye dariyar abin da Baffa ya yi wa Daddy. Shi kuwa bai tsaya ya lura da fuskokinsu ba, ya  yi tafiyarsa ya barsu a nan.

 A salube suka isa gidan suka tarar da Mommy da Amira da suka riga su isowa. Duk suna tsaye bakin kofar falon suna dakon karasowarsu.

 “Ina Baffan kuma ka baro shi”? Mommy ta tambaya.

 A sanyaye ya amsa mata da cewar “sauka yayi a hanya ya tafi. Na san kuma wajen Jibo ya koma”.

 “Surkulle fulani! Ahn ba ka san surkullen su ba ne shi ya sa hakan ya baka mamaki. Ai na gaya maka sai ka tashi tsaye ka kwato danka. Duk duniya  yana da wanda ya fika ne? kai ne ubansa na tashin alkiyama”.  Mommy ta fada.

 “Ni yanzu ban san yadda zan yi da shi ba. Kina ganin tun da aka fara zancen yaron nan, aka alakatan ni da shi har tauraruwata da ta dusashe a duniyar siyasa ta fara haskawa. Idan nagaya miki yawan membobi da  senatoci da suka kira ni, daga randa aka haskaka Baffa a Tv zuwa yau zaki yi mamaki.

 Dayawa so suke su sayi hannun jari a wan nan aikin daza su aiwatar, saboda kin san shi wan nan shugaban kasar ba wasa. Idonsa na kan wan nan aikin. Shi da kansa ya ke bibiyar komai. Shine su ke so su saka hannun jari a kamfanin don su samu riba mai tsoka.

 Ni kuma in har na taimaka suka samu cikar burinsu, nima zan ji dumus a account dina”.

 “Ai yanzu ma ba fushi zaka yi ba. ‘Da dai naka ne. Dole ka jawo abinka jikinka”, Mommy ta ce da shi.

 Ita kuwa shagwababbiyar kaya sai zunbura baki ta yi san nan cikin muryar sangarta, tace “Mommy idan aka kwato shi daga can gidan zaki hadamu aure”?

“Me zai hana autale. Ai gida bai koshi ba, ba a kaiwa dawa ba”.

 “Yeh Mommy na shi ya sa na ke sonki”

 Shi kuwa Baffa ya na isa gida, Mallam Jibo ya fito rakiyar ‘yan sannun da zuwan Baffa. Yana ganinsa ya fara murmushi kamar ba shi ne dazu ya hade rai a motar Honourable ba sai kace san layya.

 Nan dai ya tsaya yana gaisawa da abokan arziki.

 A bangaren Hamida kuwa tana hawa social media ta ci karo da abin da ya daga mata hankali. Ba komai bane sai hotunan Baffa da Sofi da ita Sofi da kanta ta yada tana nuna shine mijin da zata aura.

 Ita ba wata hira suke da Wabili ba balle ta shaida mata abin da ke zuciyarta. Kawayenta biyu a duniya Humaira da Zahra. Su kuma sai ta kasa jarumtar tattauna matsalar da su. Ganin abin ya shafi ‘dan uwansu.

 Bai samu kansa ba sai dare. Yayi kokarin kiran Hamida yadda ya saba. Wayarta a kashe. Washegari ya tura Walid ya kirata saboda har a wan nan lokacin wayarta a kashe take, Walid ya ce da shi yau da wuri ta fita, saboda ko Driver bata jira ba a napep ta tafi.

 Yawan bakin da ke shigowa ya hana shi bin ta makarantar. Ibu ne ya masa dirar sassafe. Sun yi matukar murnar ganin juna. Ana haka sai ga abin karyawa niki niki daga gidan Honourable Sofi da ta sha kwalliya ta kawo.

 Har kasa ta tsugunna ta gai da Wabili da Mallam  Jibo. Saboda haka Mommi ta sanar da ta yi saboda ta ja hankalin Baffa zuwa gareta.

 Su kuwa mamaki ne ya kashe su, na ganin yadda ta yi musu. Yarinyar da ko kallo ba su ishe ta ba, amma ita ce wai har da durkuson gaisuwa. Duk da haka ba su nuna mata komai ba, sai ma godiya da suka shiga yiwa Mommy na hidimar da ta shiga da Baffa.

 Kuloli manya guda bakwai ta ciko da abinci kala kala. Ga farfesun kafar sa dana kaji dana kayan ciki. Ga dankali da kwai da masa da gurasa. Ga kuma kunun gyada mai yawan gaske a wani flask din.

 Wabili sai budewa take tana ta kakabi. Fadi take “ga fa abinci uban masu gida. Wane za a fara zuba maka”?

 “Barshi tukunna Gwaggo. Ba yanzu zan karya ba”.

 Cikin muryar shagwaba Sofi tace “kai my Dr. please ka daure ka ci ko yaya. Mommy fa da kanta tayi maka girki”.

 Ganin yadda ya yi banza da ita Ibu ya yi saurin cewa “kar ki damu ni zan tabbatar ya ci. Bai cika cin abinci very early ba”.

 Tafi ta yi cikin murna, san nan tace “I know it. Ni na san we have a lot in common. Ni ma bana cin abinci da wuri”.

 Ibu ne ya dan jata da hira, san nan ta mike da niyyar tafiya, tana mai rokon ya kawo mata ziyara ta musamman gidansu.

 A nan ma Ibu ne ya mata alkwarin za su zo.

Tana fita Ibu ya raka ta da ido. Har da leke kamar ya ga wata sabuwar halitta. Sai da ta fita san nan ya ce “Gwaggo na ga kamar kin yi surika”?

 Dukan wasa ya kai masa. San nan ya ce “amma kai za a ba ta ba ni ba ko”?

 “Ai ko irinta hudu aka bani ba zan canza su da Humaira ta ba. By the way where is African Queen? Ban ganta ba tun da na shigo”.

 Sai da ya shafi fuskarsa, mai nuna alamun damuwa, san nan yace “I don’t know what is wrong. Tun jiya da na shigo na ke gwada wayarta a kashe. Yau da safe kuma na tamabayi Walid ya ce wai she went to school very early”.

 Wayarsa ya dauko ya bude social media, sai ga zantuttukan auren shi da Sofi suna ta yawo.

 “This could be the reason, and nima abin da ya kawo ni ke nan. Na san Hamida is the only girl in your life kuma sai na ga zancen aure da wan nan da ta kawo abinci yanzu”.

 “Amma sai na ci mutuncin yarinyar nan” Baffa ya fada a zafafe.

 “By the way who is she”? Ibu ya sake tambaya.

 “Some one not importanat at all”.

 Wabili ce da ta sake shigowa ta ke wa Ibu bayanin matsayin Sofi a wajen Baffa. Tun da suke Baffa bai taba bashi labarin yadda Honourable ya wulakanta su ba. Ya dai san labarin Humaira. Kuma iya aurenta da mijin yayarsa ya sani, amma bai san labarin dukkansa ba.

 “Gwaggo ga dukkan alamu ‘yar gida za ayi” ya fada da alamar zolaya a fuskarsa.

 Gwaggo murmushi kawai ta yi. Duk da zancen ya daki zuciyarta, saboda fuskantar inda Hamida ta sa gaba a dangantakar ta da Baffa.

 Duk da haka ba za ta zama mai son kai ba. In har Baffa ya na da burin auren Sofi ba za ta ki ba.

 Shi kuwa juyawa ya yi wajen Ibu yace “Allah ya sa African Queen ta ji ka. Sai ka san explanation da zaka bata”.

 Abba ne ya katse musu hirar da suke yi. ‘Yan kwamitin masallaci ne suka yo kungiya suka zo wa Baffa murna. Ai kuwa duk lodin abincin da Sofi ta zo da shi Baffa ya sa aka kaiwa bakin.

 Koko da kosan da Gwaggonsa ta yi masa shi ya dauka ya ci ya koshi. Sai bayan sallar la’asar ya samu saukin bakin da su ke ta zuwa, ciki kuwa har da Honourable da wasu abokansa. Nan suka ci abincin rana da Mallam Jibo, wanda mamakin sauyin Honourable ya daina ba shi mamaki sai dai dariya.

 Wabili ce ta zagaya tsohon layinsu domin barka. Ta tagar dakin Walid in da a nan ya sauka tun dawowarsa, ya hango Hamida.

 Ba yanda ba su yi ba a gyara masa karamin bangaren da ke gefen gidan. Wanda duk wanda ya gani ya san Baffa ya gina shi ne da sunan nan ne zai zamana  sashen sa, amma fir ya ki.

 Nan dai cikin gidan ya dawo ya sauka a dakin Walid. Shi kam ya kudurta, sai randa Abba ya damka masa Hamida a matsayin mata san nan su tare a sashen nasu tare da ita.

 Cikin shigarta ta kullum watau hijabi har kasa ta shigo. Sai dai sabanin lokutan baya yau sanye ta ke da nikabi da ya rufe fuskarta.

 Kamar marar gaskiya haka ta shigo falon Gwaggon, saboda so take yi ta yi sauri ta shige dakinta ba tare da kowa ya ganta ba.

 “Baki da gaskiya ne ki ke sanda”?

  A ‘dan firgice ta juyo inda ta ji sautin muryarsa. Kokarin wucewa ta fara yi amma ya sha gabanta ya hana ta wucewar.

 “Ina ki ka je da sassafe. And why did you switch off your phone”?  

 Muryarta a dashe tace “mutuwa tayi”.

 “me ya samu muryarki”.

 Shiru ta yi ba ta bashi amsa ba, saboda ta san idan ta ci gaba da Magana zai gane kukan da ta kwana ta yini tana yi, ya dasar da muryarta ta.

 Hannu ya mika mata ya ce “mu ga wayar”?

 Kin bashi tayi saboda ta san zai gane abin da ta yi.

 Jakar da ke rataye saman hijabinta ya zare. Ya bude ya dauko wayar. Abin mamaki ma a kunne take. Kiran wayar yayi tana hannusa sai a lokacin ya gane me ta yi.

 Murmushi ya yi. San nan ya ce “Hamida me na yi har na shiga call divert a wayarki”.

 Ba ta re da ta shirya ba sai kawai jin hawaye tayi ya zubo daga fuskarta.

 “Hasbunallahu wani’imal wakil. Me ya faru har da kuka”?

 Shiru tayi ba ta ba shi amsa ba. Nan tunanin abin da Ibu ya fada masa dazu ya fado masa a rai. Wayarta ta ta ya fara dubawa. Tsaf kuwa hotunan da suka bazu a social media su ne a shafin farko da ya fara budewa.

 “Is this all because of this”? nan ma shiru tayi ta kasa ba shi amsa, sai wani hawaye da ya sake wanke mata fuska. Hannunsa ya saka ya kunce nikabin da ta kulle fuskar da shi.

 Kumburin fuskarta ne ya tabbatar masa ta sha kuka sosai. “I will deal with this girl” ya fada a hasale.

 Nan dai ya samu ya rarrashe ta tare da nuna mata karya ne duk abin da ta gani. Sai da ya ga ta gamsu da bayaninsa san nan shima ya saki muryarsa yace “gaskiya baki kyauta min ba. Tun jiya kin hanamin sukuni. Pls my African Queen duk sanda kike doubting wani abu a kaina. Feel free ki tambayeni direct. Don’t just assume things”.

 Hakuri ta ba shi na zargin da ta darsa a ranta game da shi. Ibu da ya dawo daga cikin gari ya tarar da sun dinke barakar da Sofi ta yi sanadin ta, dariya ya dinga yi. Ya na fadin “ban san Fulani da saurin karaya da tsoro ba sai a kanki”.

 Dariya ta yi san nan ta kalli Baffa ta ce “Ya Baffa gaya wa wanda ya ke damunka a kan Humaira ka bashi ita ya turo ran jumma’a daurin aure”.

 “Ashe laifukan naki ban da daukin alhakin DR AMA har da kisan kai ki ke son ki yi a kai na” Ibu ya mayar mata da martanin zolayar da ta yi masa.

 Dariya kawai suka yi. Washegari kuwa jirgin safe ya bi don ya yi visiting Humaira a Abuja san nan ya wuce Lagos wajen aikinsa.





CHAPTER TWENTY SEVEN

 Lokacin da Baffa ya je halartar zaman majalisa a Abuja ya hadu da Humaira. Zahra ce kawai bai gani ba. Sun yi waya ta sanar da shi tana gidan Honourable. Saboda haka ya daura niyyar zuwa ya je ya ganta, tun da sun hana ta zuwa in da ya ke.

 Rabonsa da gidan ya haura shekara goma, amma gidan bai ‘bace masa ba. Da kafa ma ya taka tun da ba wani nisa ne da gidan da sabon gidansu ba. Ya dau kimanin awa daya kafin ya isa saboda ko ina sai ya tsaya ya gaisa da mutanen da suka zauna a tsohuwar unguwarsu.

 A sanin da ya yi wa gidan Honourable ko yaushe sabon farin fenti ke shafe a jikin katangar. Amma abin mamaki wan nan karon sai ya ga fentin ya tsufa, alamun an dan kwana biyu da yin sabon shafen.

 Bayan sun gaisa da mai gadin ya yi masa bayanin ko shi waye. Shi ma kuwa da murna suka sake sabuwar gaisuwa, saboda ya kwana biyun nan ba sunan da ya ji ana yawan ambata a gidan irin sunan sa.

 Ya nuna masa yana son ganin Zahra. Shi ya yi masa jagora zuwa bakin kofar falon. Bayan ya yi sallama ya tsaya ya na kallon harabar gidan. Shuke shuken da ya sani wadanda saboda ban ruwansu kawai aka haka borehall a gidan duk sun mutu.

 Mota daya ce a fake a inda ake ajiye mota. Itama da alama ta dan kwana biyu ana morar ta.

 Amsar sallamar da aka yi ya sanya Baffa maida hankalinsa inda yaji muryar. Zahra tana bude kofa tayi arba da yayanta. Gaba daya ta fada jikinsa ta na kuka.

 Shima murnar ganinta ya sanya shi jin wata kwalla ta dan bullo ma sa. Amma haka ya daure ya fara lallashinta.

 “To kuma kukan na menene”? Baffa ya ce da ita. Gaskiyar yafi kewarta sama da Humaira. Saboda ita ta kan kirashi duk sanda taga dama. Har kuma hotunanta ta kan aika masa.

 Sabanin Zahra da ta ke da rangwamen gata. Wayar ma sai dai a sace idan ta samu Dadin su Amal ya bata tasa ta kira mutan gidansu. Saboda haka ita tun da ya tafi bai taba ganin ko da hoton ta ba.

 Yanzu kuma yazo duk mutan gidan Honourable sun je sun gaisa da shi amma ban da ita.

 “Waye nan yake sallama ne”? muryar Amira ta katse su.

 “Ya Baffa ne ya zo”, ta amsa mata.

 Har zata ce wanene Baffa sai kuma ta tuna da DR AMA da ya dawo daga kasar waje. Tun safe take jabe waje daya. A nan Zahra ta kawo mata ruwa da roba ta yi alwala ta yi sallah duk a waje daya. Saboda tace wai ta kasa ta shi.

 Amma ta na jin Baffa ne ya zo ta yunkura ta mike tana fadin “kuma don sakarci sai ki barshi a waje a tsaye sai kace wani bako. Baffa shigo mana ka tsaya da ga waje”, inji Amira.

 Ya saba ko sanda yake zuwa kowa na wulakanta shi banda Amira. Tana martaba shi tana kuma nuna kulawar ta akan sa.

 Ita da kanta ta shigo da shi tana fadin “Zahra yi sauri ki cewa Mommy ga Baffa ya zo”.

 Ita ma Mommy da murna ta tarbe shi. Ba ta bari Zahra ta kawo masa ruwa ba. Ita da kanta ta shiga kicin ta hado masa abin tabawa. Da yake shi ma ya san kan tsiya sai ya kalleta ya ce “Mommy ki barshi. Azumi na ke yi”.

 Sun dan gaisa suka taba hira sama sama har yake tambayar Amira yaranta. Zahra ce ta kira su suka gaisa da kawunsu. Shi kansa yaran sun birge shi. Nan ya jawo su yake tambayarsu sunayensu da kuma shekarunsu.

 Mommy kuwa sai fadi take tana cewa “kazo ga mutuniyar taka ba ta nan”.

 Bai gano zancen wa ta ke yi ba bai kuma damu da tambayarta wa take nufi ba. Sai da ta ce “da Sofi ta san zaka zo ka kawo mata ziyara ba abin da zai sa ta fita”. Sai a lokacin ya gano wacece mutuniyar ta sa da Mommy ta ke fadi.

 Shi dai ganin ba za su barshi ya yi hira da kanwarsa ba ya sanya shi mikewa da nufin barin gidan. Mommy ta so dakatar da shi saboda tana son su gana da Sofi wacce ta dame ta da zancen Baffa, amma ya nuna mata sauri ya ke yi, yana da abin yi.

 Bayan Zahra ta raka shi ya ce da ita idan ta samu dama ta zo ta karbi tsarabar ta. Ba ta son ta nuna masa idan ma ta karba ba amfana zata yi da ita ba. Sai kawai ta ce ya ajiye idan ta samu lokaci zata shigo.

 Sofi kuwa ba karamin bakin ciki ta ji ba da ta dawo daga birthday party din kawarta ta tarar Baffa ya zo bai same ta ba.

Da kyar kuwa ta hakura da zuwa a daren. Ta daure akan zuwa washe gari taje ta ganshi saboda a daren wajen goma saura ta dage sai ta je gidan su Baffa.

 Tun daga wan nan rana, abincin Baffa safe, rana, dare ya koma gidan Honourable. Kullum da garar da Mommy zata shirya masa da kanta. Tun da yake Mommy ba ta taba bashi ko ruwa ya sha ba, amma yanzu ta fi kowa kokarin karrama shi.

 Haka nan Sofi za ta ci kwalliya ta dauka ta kai masa. Nan kuwa zata bata lokaci tana ta karairaiya ita ala dole ta na gaban masoyinta.

 Gwaggo kuwa ta yi ta nan nan da ita. Hamida ma daurewa kawai take idan ta zo, saboda ba ta son sabani ya sake shiga tsakaninsu da yayanta. Haka Sofi zata yi ta nanukarsa tana daukarsu hoto. Shi kuwa da ka kalli hoton ka san ba a san ransa aka dauka ba.

 Dan zagaya Zarah da ya ke sai mutan gidan Honourable suka dasa a ransu wajen Sofi ya ke zuwa.

 An dauki kamar sati biyu ana cikin wan nan kwado. Sai a wan nan rana Abba yana zaune da Sule mai shayi, wanda shima yanzu ya zama Alhaji Sule sanadin Baffa.

 Abokanan mahifinsa na kuriciya guda uku ban da Abbansa duk sai da ya kai kowa ya sauke faralli. Ya kuma kara musu makudan kudi domin kara jari ko kuma canza wata sana’ar ma gaba daya.

  A Farfadar gidan Mallam Jibo, Honourable ya same su su biyu. Bayan sun gaisa, ya bijirowa da Mallam Jibo maganar hada aure tsakanin Sofi da Baffa.

 Abba bai ji dadin maganr da Honourable ya zo da ita ba, saboda shima ya fuskanci inda Hamida da Baffa suka sa gaba.

 Amma duk da haka fillanci ba zai taba barinsa ya bara ba. Da ace Hamida a wani waje Baffa ya gano ta yana so to da kuwa sai inda karfinsa ya kare domin tabbatar da Baffa ya samu cikar burinsa.

 Kuma ko a yanzu ba shi da tabbacin Baffa ba ya son diyar Honourable. Hakan ya dada sanya shi amsawa Honourable da cewar “ai Yaya duk hukunci da ka yanke akan uban masu gida dai dai ne. Allah ya sanya alkhairi”.

 Sule mai shayi ne ya yi katsalandan. Duk sun san irin abin tsiyar da Honourable da iyalansa suka shukawa Baffa. Saboda haka ya yi tsagal ya ce “duk da haka ka san halin dan yau. Da dai an tuntube shi an ji ta bakinsa ko don a fita hakkinsa. Kuma ……..”

 “Ka ga don Allah dakata mallam” Honourable ya katse shi da sauri. San nan ya ci gaba da cewa “idan kai irin tarbiyar da kakewa yaranka ke nan na kar su yi maka biyayya akan abin da ka zaba musu ni ba haka nawa tsarin ya ke ba. Da Baffa da Sofi duka ‘ya’yana ne. kuma yadda na ga dama haka zan zartar da hukunci da na so a kansu”.

 Zai sake Magana, sai Mallam Jibo ya yi masa alama da yabar zancen haka nan. A fusace ya mike ya na fadin “Idan ya zo ka tura min shi saboda ba na a son abin ya dauki lokaci. Kuma tun da duk abin gida daya ne ba wani bincike za a tsaya yi ba.

 Yarinya ce ta san shi ya santa. Duk kuma nine waliyyinsu. Idan na yanke ranar auren zan sanar da kai. Ko ba komai kai aminin mahaifinsa ne. Ba kuma zan kewaye ka saboda kasa ta rufe idon dan uwana in ce zan yi wani abu ban sanar da kai ba”.

 “Hakane Yaya. Allah dai ya sanya alkhairi” Mallam Jibo ya fada a lokacin da ya mike domin ya yi masa rakiya.

 Bayan ya shiga gida yake sanarwa da Wabili abin da ya kawo Honourable gidansa. Kuka ne ya kwace mata na ganin tashin hanklin da ya tunkaro diyarta. Duk da ba ta sanar da ita ba kiri kiri, amma duk wanda ya ga mu’amalarsu da Baffa ya san akwai kauna mai tsanani a tsakaninsu.

 Sai da ta share hawayen da ya zubo mata san nan ta ce “Mallam anya idan aka yiwa Baffa haka, ba’a kware shi ba. Ni na san hankalinsa ya karkata ga Hamida. Yanzu kuma ga wan nan maganar Yaya ya bullo da ita.

 A duba da kyau yaran abin a tausaya musu ne saboda sun shaku da juna”. “Kin ga ki daina damuwa. Kin taba ganin dan Adam ya yai abin da Allah bai hukunta ba”?

 “Na sani Mallam bari shi Baffan ya dawo mu ji ta bakinsa”.

 “Yawwa haka nake son ji. Kuma ki duba da kyau. Ba na son ki yi kokarin cusa masa ra’ayi ko da da shagube ne. Haka zalika kar ki nuna masa kin fahimci yana son Hamida. Ki bar shi ya zabi ra’ayinsa”.

 A haka suka tsaya. Shi kuwa Baffa ya na can yana ta fafutukar hada wasu takardu domin komawa Japan. Hutun da suka ba shi ya kare, amma da yake shi ne wakilin kamfaninsu a Nigeria, sai ya ke jifan tsuntsu biyu da dutse daya.

 Yana tare da su Abbansa da kuma Hamidansa, san nan kuma yana aikin da aka shi. Shi ya sa yake ta zarya tsakanin Abuja da Kano.

Comments

Popular Posts